Muhallinka Rayuwarka
Wayar da kan jama’a da ilmantar da su, game da sha’anin da ya shafi Noma da muhalli da canjin yanayi. Yin bayanai dangane da batun gurbacewar yanayi tare da dumamarsa (Yanayi).
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
Yadda sauyin yanayi ke haddasa wutar daji da kafewar koguna sakamon tsananin zafi
Shirin Muhallinka rauwarka tare da Nasiru Sani ya mayar da hankali ne kan sauyin yanayi wanda ya haddasa tsananin zafin da yanzu haka ya addabi kasashe da dama musamman a yankunan Turai nahiyar Asiya da kuma Afrika wada tuni ya haddasa gagarumar illa ta hanyar kafar da tarin koguna a mabanbantan yankuna.07/10/202319:56 -
Hasashen daukewar damuna da wuri na shirin haddasa matsala ga Manoman Najeriya
Shirin Muhallinka rayuwarka tare da Nasiru Sani a wannan mako ya mayar da hankali ne kan hasashen masana kan yiwuwar daukewar ruwan damuna da wuri a wasu sassan Najeriya, lamarin da zai haddasa gagarumar matsala a tsarin samar da abinci.23/09/202319:49 -
Tsadar taki ya haddasa koma baya a harkokin noma a Najeriya
Shirin 'Muhallinka Rayuwarka' na wannan mako zai yi duba ne kan batun matsalar takin zamani da manoma ke fama da shi a Najeriya shekara da shekaru, duk da cewa tsadar takin na bana ba irin wadanda aka saba gani a baya bane.16/09/202320:00 -
Kamaru ta sako ruwan madatsar lagdo wanda ya janyo asarar kama daga rayuka da dukiyoyi
A yau shirin zai bada hankali ne akan sakin ruwan madatsar ruwan lagdo da kamaru zata yi, wanda yanzu haka mazauna wasu yankuna da ruwan zai kwaranya ta cikin su a Najeriya ke cikin tashin hankali dangane da irin asarar kama daga ta rayuka har ya zuwa ta dukiyoyi.A karshe dai, gwamnatin Nigeria, ta tabbatar da cewa makwabciyarta Kamaru, ta sako ruwan da ke tumbatsa daga cikin madatsar ruwan Lagdo, lamarin da kan kasancewa babbar barazana ga dunbin al’ummomin Nigeria.09/09/202319:29 -
Rawar da mata ke takawa a bangaren noma a Najeriya
A yau Shirin zai karkata ne a kan yadda mata ke taka muhimmiyar rawa a bangaren noma a Najeriya kuma kasancewar su a harkar noman na ba da gudunmawa ta bangrarori da dama.Manoma mata a tarayyar Nigeria, na taka rawar a zo a gani a fannin habaka samar da abinci don amfanin al’ummar kasar.20/08/202319:57 -
Bankin raya Afirka na shirin tallafawa manoma a Najeriya
Shirin ya karkata ne akan wani shirin tallafawa manoma a Najeriya wanda Bankin raya Afirka ke tallafawa kan yadda za’a samu inganci da habakar samar da wadataccen abinci a fadin kasar wato agricultural transformation agenda support program karkashin ma’aikatar noma ta kasar wanda aka kaddamar a garin Bunkuren jihar Kano.13/08/202319:32 -
Muhallinka Rayuwarka: Matakin gwamnatin Najeriya kan samar da abinci
Shirin "Muhallinka Rayuwarka" a wannan makon tare da Nasiru Sani ya duba dokar ta baci da gwamnatin Najeriya ta sanyawa bangaren abinci, domin kaucewa fadawa karancin abinci.22/07/202319:48 -
Matsalar zaizaiyar kasa na ciwa mazauna birnin Calabar tuwo a kwarya
Shirin "Muhallinka Rayuwarka" a wannan makon ya yi duba ne kan matsalolin zaizayar kasa, da ke samu a yankin Niger Delta da ke shiyar kudu maso kudancin Najeriya. Jahar Cross River na daya daga cikin jahohin da ke fama matsalar musamman a wani bangare na babban birnin ta Calabar.24/06/202319:01 -
Shiri na musamman kan yadda ake amfani da fasahar AI a bangaren noma da kiwo
Shirin 'Muhallinka Rayuwarka' a wannan karon ya yi nazari ne kan yadda a yanzu ake amfani da Kirkirarriyar Basirar Ai a bangaren noma da kiwo musamman a wannan lokaci da ake kokarin wadata duniya da abinci.18/06/202319:32 -
Karancin ruwan sama da yadda noman masara ke fuskantar kalubale
Shirin "Muhallinka Rayuwarka" a wannan lokaci ya mayar da hankali ne kan matsalar karancin ruwan sama da yankin karamar hukumar Wase ta jihar Filato ke fuskanta wanda yanzu haka manoma da masu kiwo ke cikin halin dar dar, sannan kuma da wata matsalar da manoman masara ke fuskanta a jihar Kano duk da ke yankin arewacin Najeriya.11/06/202320:48 -
Akwai yuyuwar samun ambaliyar ruwa a Najeriya a daminar bana-NIMET
Hukumar kula da hasashen yanayi ta tarayyar Nigeria NIMET, ta ankarar da mazauna wasu jihohin arewacin kasar dangane da mamakon ruwan saman da ake sa-ran zubawa nan da ‘yan kwanaki masu zuwa.04/06/202319:54 -
Yadda tsananin zafin rana ke wa jikin dan adam illa
Shirin "Muhallinka Rayuwarka" ya yi dubi ne kan yadda ake fama da zafin rana a Afirka, ciki har da Arewacin Najeriya wanda yanayin kan kai sama da maki 40 na ma’aunin sa.28/05/202319:43 -
Matsalar bacewar wasu nau'in itatuwa a yankunan mu
A cikin shirin muhalinka rayuwar ka Nasiru Sani ya mayar da hankali a kan daya daga cikin matsaloli na bacewar iatatuwa a wasu yankuna,al'amarin da ya kai hukumomi daukar mataki na samar da shirin sake shuka irin wadanan uiatce tare da goyan bayan kungiyoyi.Nasiru Sani ya jiyo ta bakin masana da masu ruwa da tsaki dangane da wannan matsala.20/05/202321:30 -
MDD- Kudin da ake kashewa wajen sayen ruwan roba ya kai ayi amfani dasu wajen samar da ruwan sha
A wannan shirin na Muhallin ka Rayuwar ka, shirin dake tattauna wa da masu ruwa da tsaki kan sauyi ko dumamar yanayi da kuma uwa uba fannin noma da kiwo, wanda Nasiru Sani ke jagoranta.Shirin na wannan mako zaiyi dubi ne kan wani rahoto da Majalisar dinkin duniya ta bayana cewar kudin da ake kashewa wajen sayen ruwan roba ya kai ayi amfani dasu wajen samar da wadataccen ruwan sha a fanfunan daukacin al’uma a duniya.13/05/202319:39 -
Bikin dashen itaciyar Kuka a garin Kwanni na jamhuriyyar Nijar
Shirin Muhallinka Rayuwarka tare da Nasiru Sani a wannan makon ya mayar da hankali kan shirin dashen itaciyar kuka da ya gudana a garin kwanni da ke jamhuriyar Nijar wanda Salisu Hamisu ya halarta don jin yadda shirin ya gudana tare da burin da ake da shi har ya kai ga baiwa itaciyar ta kuka muhimmanci a wannan yanki kuma a wannan karo.26/03/202318:41
Muhallinka Rayuwarka
Wayar da kan jama’a da ilmantar da su, game da sha’anin da ya shafi Noma da muhalli da canjin yanayi. Yin bayanai dangane da batun gurbacewar yanayi tare da dumamarsa (Yanayi).