Isa ga babban shafi
Muhallinka Rayuwarka

Akwai yuyuwar samun ambaliyar ruwa a Najeriya a daminar bana-NIMET

Wallafawa ranar:

Hukumar kula da hasashen yanayi ta tarayyar Nigeria NIMET, ta ankarar da mazauna wasu jihohin arewacin kasar dangane da mamakon ruwan saman da ake sa-ran zubawa nan da ‘yan kwanaki masu zuwa.

File photo of a house partially submerged in flood waters is pictured in Lokoja city, Kogi State, Nigeria, September 2018.
File photo of a house partially submerged in flood waters is pictured in Lokoja city, Kogi State, Nigeria, September 2018. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

A cewar hukumar, wacce kan yi hasashen yadda yanayi zai kasance a kasar, tuni na’urorinta suka hango alamomin tsawa da walkiya a yankunan jihohin Borno, Taraba, Gombe, Bauchi da  kuma Kano.

Wannan hasashe na zuwa ne yayinda har yanzu, wasu al’ummomin kasar, ba su gama farfadowa daga barnar da ambaliya ta yi musu a daminar bara ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.