Jiragen yakin Turkiya sun kashe mayakan kurdawa 26 a Iraki da Syria
Wallafawa ranar:
Talla
Turkiya ta ce jiragen yakinta sun yi nasarar halaka mayakan Kurdawa 26 yayin hare-haren da suka kai a cikin kasar Syria, da wasu yankunan arewacin kasar Iraqi, farmakin da ta ce martani ne akan sojojinta 12 da mayakan kungiyar PKK suka kashe a karshen makon jiya a Iraqi.
Bayanai sun ce, jami’an tsaron kasar ta Turkiya sun kuma cafke gwamman masu fafutukar goyon bayan kungiyar ta PKK da turkiya ayyana a matsayin kungiyar ‘yan ta’adda, tun bayan hare-haren da ta kaddamar da zummar neman kafa yantaciyar kasar Kurdawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu