Isa ga babban shafi

Iran ta sake musanta zargin cewa tataimakawa Rasha da makamai

Iran ta nisanta kan ta daga cikin kasashen da ke baiwa Rasha makamai da za ta yi amfani da su a yakin Ukraine, kasar da sojojin Rasha suka mamaye.

Wasu daga cikin makaman Iran da ake kyauatata zaton ta taimakawa Rasha da su
Wasu daga cikin makaman Iran da ake kyauatata zaton ta taimakawa Rasha da su AFP - -
Talla

kyiv da kawayenta na Yamma suna zargin Moscow da yin amfani da jirage marasa matuka da Iran ta kera wajen kai hare-hare kan Ukraine a makonnin da suka gabata. A  litinin ake sa ran za a tattauna batun a taron ministocin harkokin wajen kungiyar tarayyar turai a Luxembourg.

Ministan harkokin wajen Iran Hossein Amir-Abdollahian ya musanta zargin da ake masa, ya kuma ce kasarsa ba ta bayar da  makaman da za a yi amfani da su a yakin Ukraine ba, a cewar wata sanarwa da ma'aikatarsa ​​ta fitar.

A ranar Litinin da ta gabata, shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce an kai hare-hare da dama da ya ce ta hanyar amfani da makamai masu linzami na Iran da jirage marasa matuka, tare da aukawa makamashin Ukraine.

A wata ganawa ta daban da shugaban diflomasiyyar Turai Josep Borrell, Mr. Amir-Abdollahian ya jaddada matsayin Iran a hukumance kan yakin Ukraine.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.