Isa ga babban shafi

Nijar ta ce Faransa ta jibge makamai a wasu kasashe kusa da ita don yakar ta

Gwamnatin sojin Jamhuriyar Nijar ta zargi Faransa da  tara makamai tare da jibge dakarunta a wasu kasashe da ke makwaftaka da kasarsu da zummar kai musu hari.

Janar Abdourahamane Tiani, shugaban gwamnatin sojin Njar.
Janar Abdourahamane Tiani, shugaban gwamnatin sojin Njar. © AFP
Talla

 

A ranar Asabar ce kakakin gwamnatin sojin Nijar, Kanar Manjo Amadou Abdramane ya bayyana a wata  sanarwa cewa Faransa na ci gaba da jibge  dakaru a wani Shirin da take yi da  kunggiyar ECOWAS don kai wa  kasar hari, inda  ya  ce ta tara jiragen yaki, da jirage masu saukar ungulu, da kuma motoci masu sulke guda 40 a kasashen Ivory Coast da Jamhuriyar Benin.

Kasar da ke yankin Sahel ta shiga takun saka da Kungiyar  Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka, wato ECOWAS tun bayan da kungiyar ta yi barazanar yin amfani da karfi idan diflomasiyya  ta gaza, a kokarin da take na maido da Mohamed Bazoum kan mulki.     

A ranar 3 ga watan Agusta ce gwamnatin sojin Nijar ta soke yarjejeniyar  soji da ke tsakaninta da Faransa, wadda ke da dakaru kimanin dubu 1 da dari 5 a kasar da ta jibge don taimakawa a yakin da ake da ta’addanci.

Dangantaka tsakanin Faransa da Jamhuriyar Nijar ta yi tsami tun bayan da sojoji suka kifar da gwamnatin Mohamed Bazoum a watan Yuli.

Faransa ta ki amincewa  da gwamnatin sojin Nijar, inda ta ayyana ta a matsayin haramtacciya, tana kuma kira su mayar da Bazoum karagar mulki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.