Isa ga babban shafi

Zanga-zangar neman ficewar sojojin Amurka daga arewacin Nijar

Dubban jama'a a Jamhuriyar Nijar sun gudanar da zanga-zangar neman ficewar sojojin Amurka daga arewacin kasar a jiya Asabar, bayan da gwamnatin mulkin soja a Yamai ta ce ta janye daga yarjejeniyar soji da ta kulla da Amurka.

Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar Janar AbdurRahmane Tiani tare da mukarrabansa a birnin Yamai.
Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar Janar AbdurRahmane Tiani tare da mukarrabansa a birnin Yamai. REUTERS - STRINGER
Talla

Rahotanni daga birnin na Yamai,na nuni cewa dalibai da wasu daga cikin manyan jami'an gwamnatin soji na daga cikin mutanen da suka taru a gaban hedikwatar majalisar dokokin kasar da ke birnin Yamai.

Dubban matasa a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar
Dubban matasa a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar © AP - Sam Mednick

Korar dakarun kasashen waje,ba wani sabon abu ba ne a Nijar, an kori sojojin Faransa a karshen shekarar 2023, yanzu haka kusan sojojin Amurka 1,000 ne suka kasance a garin Agadez da ke arewacin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.