Isa ga babban shafi

Nijar ta kori jakadunta dake Amurka da Faransa da Togo da kuma Najeriya

Shugabannin juyin mulki a jamhuriyar Nijar sun sanar da kawo karshen wa’adin ayyukan jakadun su a wasu kasashe hudu a kasar da yammacin ranar Alhamis yayin da suke fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya na maido da zababben shugaban da suka hambarar a makon jiya.

Dandazon masu zanga-zangar goyon bayan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar. 3/08/23
Dandazon masu zanga-zangar goyon bayan sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar. 3/08/23 REUTERS - STRINGER
Talla

A cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na kasar, sun dakatar da ayyukan manyan jakadun kasashen Faranasa da Amurka da Najeriya da kuma Togo da Jamhuriyar Nijar.

Majalisar mulkin sojan dai na fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya na ganin ta maido da hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum, inda kungiyar kasashen yammacin Afirka, karkashin jagorancin shugaban Najeriya Bola Tinubu ta yi barazanar yin amfani da karfin tuwo don kwato mulki.

Martani

Rundunar sojan ta kuma yi barazanar mayar da martani nan take ga duk wani "yunkuri na zalunci kan gwamnatinsu."

Yayin da makwabtanta Maji da Burkina Faso suka yi gargadi kan daukar duk wani mataki na soja a kan Nijar, wanda suka ce zai daidai da shelanta yaki a kansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.