Isa ga babban shafi
Nijar

Masana sun ja hankalin Gwamnatin Nijar kan tattalin arziki

Yayin da shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou, ke cewa tattalin arzikin kasar yana bunkasa, kuma zai dore cikin wannan hali nan da shekaru biyar masu zuwa, wasu masu nazari na ganin bayanan sun saba da halin da jama’ar kasar ke ciki na matsi.

Shugaban Jamhuriyyar Nijar Mahamadou Issoufou
Shugaban Jamhuriyyar Nijar Mahamadou Issoufou atlasinfo
Talla

Abdu Dan Neto na wata kungiyar farar hula da ke Maradi, ya ce har yanzu da dama daga cikin jama’a a Nijar suna fama da yunwa, ga kuma rashin kudi a hannun mutane wadanda suka hada da ‘yan kasuwa da ma’aikata.

Yayin da yake tattaunawa da sashin Hausa RFI, Abdu dan Neto ya kamata Gwamnatin Nijar ta sake nazari kan matakin da ta ce ta dauka na tsuke bakin aljihun ta domin saukakawa mutane halin da suke ciki.

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.