Dandalin Siyasa
Shirin Dandalin Siyasa, yana tattaunawa tare da tafka muhawar kan al’amurran siyasa da ke faruwa a kasashen duniya, da batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, wanda Bashir Ibrahim Idris ke jagoranta. Wannan Shirin na zuwa ne a karshen mako Ranar Assabar da maimaci a ranar Lahadi a Shirye Shiryen Safe da Yamma.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
Rashin kasancewar mata a fagen siyasar Najeriya
A cikin shirin dandalin siyasa,Bashir Ibrahim Idris ya samu tattaunawa da wasu mata dangane da rashin samun mata a fagen siyasar Najeriya,wasu daga cikin yan kasar mata musaman sun bayyana aniyar su ta kasancewa daga cikin yan takara a zaben shekarar 2019.14/11/201810:58 -
Tasirin Na'urar Tantance Kuri'u a zaben Najeriya
Sashen Hausa na RFI na farin cikin gabatar muku da sabon shirin Dandalin Siyasa da zai rika nazari game da al'amuran da suka shafi siyasar Najeriya, Nijar, Afrika da sauran kasashen duniya. Shirin na makon farko tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari ne game da tasirin na'urar tantance masu kada kuri'u a zaben Najeriya, abin da masana ke cewa, ta na taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar magudi.08/11/201810:04 -
Jam'iyar MPN kishin kasa a jamhuriyar Niger ta kori manyan jigajiganta 13
Shirin dandalin siyasa na wannan mako, ya tabo batutuwan da suka shafi dalilin da ya hana shugaba Buhari zuwa Bauchi, ya kuma leka jamhuriyar Nijar inda jam'iyar MPN Kishin kasa ta kori wasu manyan jiga-jiganta su 13, a sha saurare lafiya.31/12/2016 -
Dalilin yin watsi da jekadun Buhari a Majalisar Dattijai
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game da batun yin watsi da amincewa da jekadu 46 da Majalisar Dattiajan Najeirya ta yi da rikicin shugabannin Jamiyyar PDP mai adawa a Najeriya da ta dare gida biyu inda wasu ‘yan jam’iyyar ke neman a raba-gari wasu kuma ke bukatar sake lale.19/11/201620:09 -
Sharhi akan nasarar Trump
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna game sakamakon zaben Amurka inda masana suka yi sharhi akan nasarar da Donald Trump dan takarar Republican ya samu bayan ya doke abokiyar takararsa Hillary Clinton ta Democrat.14/11/201620:17 -
Manufofin Clinton da Trump a zaben Amurka
Shirin Dandalin Siyasa ya yi nazari ne game da 'Yan takarar shugabancin Amurka guda biyu Donald Trump na Republican da Hillary Clinton da Democrat tare da tattauna manufofinsu. Sannan shirin ya yi tsokaci akan tasirin zaben Amurka ga Afrika.08/11/201620:01 -
An ci mutunci da zage-zage a Siyasar Amurka
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna ne akan dambarwar siyasar Amurka inda ya rage kwanaki a kada kuri’ar zaben shugaban kasa. A cikin shirin za a ji yanayin zaben Amurka da kuma yadda zaben na bana ya zo da sabbin abubuwa da ake ganin sun sabawa demokuradiyar kasar.31/10/201620:04 -
Jihohin da Abacha ya kirkiro sun yi shekaru 20
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna ne game da bikin cika shekaru 20 da jihohi 6 suka gudanar wadanda Marigayi Janar Sani Abacha ya kirkiro a shekarar 1996. Shirin ya mayar da hankali a Jihohin Gombe da Zamfara. Shin kwanliya ta biya kudin sabulu? Sannan shirin ya tabo muhawarar da ake a Majalisar Dattijai kan wani kudirin doka na Daidaiton jinsi wato kudirin doka da zai ba mata damar yin kafada da kafada da maza wanda ke yin karo da addini.15/10/201620:04 -
Shirin Zabe a Ghana
Shirin Dandalin Siyasa ya yi nazari kan shirin babban zaben kasar Ghana da za a gudanar a watan Disemba. Shirin kuma ya leka Najeriya game da batun fasa kwan da Hon Abdulmumin Jibril ke yi a Majalisar dokokin kasar.09/10/201620:07 -
Sabon rikici a majalisar wakilan Najeriya
Shirin ya mayar da hankali kan sabon rikicin da ya kunno kai a majalisar wakilan Najeriya, sakamakon tsige shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar Hon. Abdulmumin Jibril, wanda shi kuma ya rika fitar da wasu bayanan sirri na yadda ake almundahana yayin tsara kasafin 2016 a zauren majalisar.31/07/201620:04 -
Takun-saka tsakanin Saraki da Buhari
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna ne akan takun-sakar da ake yi tsakanin bangaren shugabannin Majalisar Dattijan Najeriya da kuma bangaren zartarwa musamman game da shari'ar da ake yi akan Sanata Bukola Saraki da Mataimakinsa.03/07/201619:53 -
Dandalin siyasa na yau asabar zai yo dubi kan rikicin shugabanci a jam'iyyar PDP a Najeriya
A cikin shirin dandalin siyasa Abdoulkarim Ibrahim yayo dubi dangane da rikicin shugabanci da ya kaure a jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya.Ya kuma dubo wasu labaren daga Kano dama Bauchi Najeriya.19/06/201621:06 -
Karin Farashin Fetir a gwamnatin Buhari
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna kan karin farashin fetir da gwamnatin APC ta Muhammadu Buhari mai da'awar canji a Najeriya ta yi. Shirin ya ji ra'ayin 'Yan Najeriya da bangaren adawa da kuma masana tattalin arziki kan yadda suka kalli matakin karin farashin bayan janye tallafin mai.16/05/201620:32 -
Takun saka tsakanin gwamnati da Fararen hula a Nijar
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna ne kan takun sakar da aka soma tsakanin gwamnati da kungiyoyin fararen hula a Nijar kan sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar a watan Maris.08/05/201621:05 -
Sabani akan kasafin kudin Najeriya
Shirin Dandalin Siyasa ya tattauna kan sabanin da ake samu tsakanin bangaren Zartarwa da Majalisar Dokokin Najeriya a game da Kasafin Kudi wanda har yanzu Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ki sanya wa hannu.02/05/201640:25
Dandalin Siyasa
Shirin Dandalin Siyasa, yana tattaunawa tare da tafka muhawar kan al’amurran siyasa da ke faruwa a kasashen duniya, da batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, wanda Bashir Ibrahim Idris ke jagoranta. Wannan Shirin na zuwa ne a karshen mako Ranar Assabar da maimaci a ranar Lahadi a Shirye Shiryen Safe da Yamma.