Isa ga babban shafi
Nijar-Zabe

Gidan wakilin RFI sashen Faransanci ya gamu da fishin masu zanga-zanga a Nijar

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar sun ce masu zanga zanga suka kona gidaje da shagunan jama’a da dama ciki har da gidan wakilin sashin faransanci na Radio France International Rfi a birnin Yamai,  Musa Kaka.

Masu boren adawa da sakamakon zabe a Jamhuriyyar Nijar.
Masu boren adawa da sakamakon zabe a Jamhuriyyar Nijar. AFP - ISSOUF SANOGO
Talla

Kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya shaida yadda masu zanga-zangar fiye da 200 suka yiwa gidan wakilin na RFI Musa Kaka dirar mikiya a jiya Alhamis tare da kwasar ganima baya ga kone daukacin gidan.

Wannan dai na matsayin  jerin tashe-tashe hankulan Zabe da Nijar ba ta saba gani ba a tarihi, dai dai lokacin da a karon farko farar hula karkashin mulkin Demokradiyya ke Shirin mika Mulki ga zababben shugabar farar hula a kasar  

Musa Kaka da ke matsayin wakilin Rfi na tsowon lokaci a Jamhuriyar ta Nijer, ya taba share kusan shekara garkame a gidan yari daga 20 ga watan  Satumban 2007 zuwa  23 ga watan Yulin 2008 sakamakon zargin da gwamnatin marigayi Tanja Mammadu ta yi masa  cewa, yana da alaka da ‘yan tawayen abzinawan yankin arewacin kasar.

Tuni dai hukumar gudanarwar RFI ta mayar da martani cewa, an kai wa wakilin na ta hari ne a matsayinsa na dan jarida, wanda hakan ke zama mummunan taka ‘yancin aikin jarida.

Hukumar gudanarwar RFI da ke bayyana goyon baya ga ma’aikacin na ta, ta kuma yi tir da aika-aikar yayinda ta sha alwashin ci gaba da kare ‘yancin aikin samar da labarai a Duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.