Isa ga babban shafi
Mali-Zabe

Jam'iyyun adawa sun shirya kalubalantar sakamakon zaben Mali

Wasu 'yan takaran zaben shugaban kasar Mali da akayi a karshen mako sun bayyana aniyar su ta kalubalantar sakamakon zaben a kotu saboda abinda suka kira tafka magudi da akayi.

A ranar Juma'a mai zuwa ce ake saran bayyana sakamakon zaben mai cike da sarkakiya.
A ranar Juma'a mai zuwa ce ake saran bayyana sakamakon zaben mai cike da sarkakiya. REUTERS/Luc Gnago
Talla

Wani taron manema labarai da 'yan takaran suka kira cikin su harda tsohon ministan kudi Soumaila Cisse da dan kasuwa Aliou Diallo, sun bayyana cewar ba za su amince da sakamakon zaben da ake saran bayyana shi ranar juma’a ba.

Daraktan yakin neman zabem Cisse, Tiebile Drame ya ce suna da shaidar da ke nuna musu cewar akwai kauyen da ke da mutane 150 amma kuma mutane 3,000 sun kada kuri’a acan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.