Isa ga babban shafi
Mali

An fara kidayar kuri'un zaben shugabancin Mali

An fara aikin tattara sakamakon zaben shugaban kasa zagaye na farko da aka gudanar ranar Lahadi, 29 ga watan Yuli na 2018, a kasar Mali.

Cecile Kyenge, shugabar tawagar kungiyar tarayyar turai da ke sa ido kan zaben Mali, a tsakiyar jami'an hukumar zaben kasar, yayin da suka soma kidayar kuri'un da aka kada a birnin Bamako. 29 ga watan Yuli, 2019.
Cecile Kyenge, shugabar tawagar kungiyar tarayyar turai da ke sa ido kan zaben Mali, a tsakiyar jami'an hukumar zaben kasar, yayin da suka soma kidayar kuri'un da aka kada a birnin Bamako. 29 ga watan Yuli, 2019. REUTERS/Luc Gnago
Talla

‘Yan takara 23 ne suka fafata da shugaban kasar mai ci Ibrahim Boubacar Keita.

Bayanai na nuni da cewa zaben ya gudana cikin tsanaki a cikin manyan birane. Sai dai mahara sun harba makamai masu linzami kan garin Aguelhok da ke arewacin kasar.

A garin Lafia da ke yankin Timbuktu kuwa wasu gungun mutane ne sun kone kayayyakin zabe, sakamakon wata hatsaniya da ta tashi.

Tcheble Drame shi ne shugaban jam’iyyar adawa ta URD, kuma ya ce akwai daruruwan rumfuna da ba a gudanar da zabe a cikinsu ba.

00:39

Tcheble Drame shugaban jam’iyyar adawa ta URD a Mali

Nura Ado Suleiman

Souma’ila Cisse, tsohon ministan kudin Mali, shi ne babban abokin hamayyar shugaba Boubacar Keita a zaben na bana, wanda ya yi rashin nasara a zaben shugabancin kasar ta Mali da ya gudana a shekarar 2013 da gagarumin rinjaye.

Idan har aka kammala kidayar kuri’un da aka kada kuma babu dan takarar da ya lashe sama da kashi 50, za a sake gudanar da zaben shugaban kasar zagaye na biyu a ranar 12 ga watan Agusta mai zuwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.