Isa ga babban shafi
WASANNI - afcon

Mane ya taimawa Senegal zuwa wasan karshe na AFCON a Kamaru

Kasar Senegal ta tsallaka zuwa matakin wasan karshe na gasar cin kofin Afrika da ke gudana a yanzu haka a kasar Kamaru, bayan ta lallasa Burkina Faso da kwallaye uku da 1 a fafatawar da suka yi daren Laraba a filin wasa na Ahmadu Ahidjo da ke birnin Yaounde.

Dan wasan gaba na tawagar Senegal Sadio Mané yayin wasan da kasar ta lallasa Burkina Faso da ci 3-1 kuma ta haye wasan karshe na neman cin kofin Afirka a Kamaru. 02/02/2022.
Dan wasan gaba na tawagar Senegal Sadio Mané yayin wasan da kasar ta lallasa Burkina Faso da ci 3-1 kuma ta haye wasan karshe na neman cin kofin Afirka a Kamaru. 02/02/2022. © Pierre René-Worms/RFI
Talla

Abdou Diallo da Isrissa Gana Gueye da kuma Sadiyo Mane suka taimakawa tawagar Senegal zuwa matakin karo na biyu a jere, kuma na 10 a tarihinta.

Burkina Faso

‘Yan wasan Burkina Faso dai sun nuna kansu a matsayin matasa masu hazaka da kuma sha'awar sanya farin ciki ga magoya bayansu a kasar da ke cikin tashin hankali bayan hambarar da shugaba Roch Marc Christian Kabore a wani juyin mulkin da sojoji suka yi a makon jiya.

Lions Taranga

Tawagar Lions Taranga dake matsayi na daya a jadawalin FIFA wajen iya taka leda a Afirka, na jiran daya daga cikin kasashe biyu da zasu fafata anjima domin sanin da wa zata kara wasan karshe a ranar Lahadi, tsakanin Kamaru mai masaukin baki da kuma Masar wacce ba kanwar lasa ba ce a harkar tamola.

CAF

To, hukumar kwallon kafar Afirka CAF ta sauya lokacin da ya kamata a doka wasan neman matsayi na uku na gasar cin kofin Afirka

CAF ta maido da lokacin ne zuwa ranar Asabar Mai zuwa tsakanin Burkina Faso da ko Masar ko Kamaru (za’a gane bayan wasansu na wannan Alhamis) maimakon Lahadi ranar da ake doka wasan karshe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.