Isa ga babban shafi
Wasanni

TikTok ya shiga jerin masu daukar nauyin gasar AFCON

Kamfanin TikTok ya sanar da kulla yarjejeniyar kasuwanci ta tsawon shekara guda da hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF.

Tambarin kamfanin TikTok
Tambarin kamfanin TikTok Kirill KUDRYAVTSEV AFP
Talla

Matakin ya sanya kamfanin shiga jerin masu daukar nauyin gasar cin kofin kasashen Afirka da ake shirin farawa a kasar Kamaru.

A karkashin wannan yarjejeniya dai, TikTok, sabon dandalin da yayi fice wajen wallafa takaitattun hotunan bidiyo zai kasance cikin masu daukar nauyi da kuma tallata kansa a gasar cin kofin Zakarun kungiyoin kasashen Afirka a shekarar bana, da kuma gasar cin kofin kasashen Afirka ajin mata da kasar Morocco za ta karbi bakunci a tsakanin 2 zuwa 23 ga watan Yulin shekarar 2022 da muke ciki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.