Isa ga babban shafi

Ana dakon hukuncin kotun Ecowas dangane da karar jagoran yan Adawar Nijar

Ranar talata 31 ga watan Mayu ne kotun tsarin mulkin kasa ta kungiyar kasashen Ecowas dake Abuja zata zartas da hukunci dangane da karar da  jagoran yan adawa a Jamhuriyar Nijar Mahamane Ousmane, Shugaban jam’iyyar RDR Canji ya shigar.

Mahamane Ousmane tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar kuma dan takarar shugaban kasa a yanzu.
Mahamane Ousmane tsohon Shugaban Jamhuriyar Nijar kuma dan takarar shugaban kasa a yanzu. RFI
Talla

Shugaban jam’iyyar RDR Canji Mahamane Ousmane ya kalubalanci nasarar shugaban kasar Bazoum Mohammed dangane da sakamakon zaben shugabancin kasar na watan Fabarairun zagaye na biyu.

 Jam’iyyar RDR Canji ta bayyana cewa an tafka magudi,inda take kalon jam’iyyar PNDS a matsayin wacce ta shirya haka,banda magudin an samu tashin hankali a wasu wurare.

Za a dai gudanar da wannan zama a Abuja dake birnin Tarryar Najeriya a karkashin shugabancin alkalai da suka hada da  Edouard Amoako Asante,Dupe Atoki da Januaria Tavares Silva Moreira Costa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.