Isa ga babban shafi
Nijar

Mayakan Boko Haram sun mika kansu a Nijar

Mayakan Boko Haram 31 sun mika kansu ga hukumomin Jamhuriyar Nijar kamar yadda ministan cikin gidan kasar, Bazoum Mohamed ya sanar.

Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi sun kaddamar da shirin kakkabe Boko Haram
Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi sun kaddamar da shirin kakkabe Boko Haram REUTERS/Joe Penney/
Talla

Ministan ya ce, mayakan sun kuma mika makamansu a yankin Diffa da ke kudu maso gabashin kasar, kuma a karon farko kenan da mayakan suka yi haka a kasar.

Majiyar tsaro ta shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, a halin yanzu an killace mayakan a wuri guda don ba su horon da zai sauya tunaninsu  kafin daga bisani su koma ga iyalansu.

Tun a cikin watan Fabairun shekarar 2015 ne, kungiyar Boko Haram ta tsananta kaddamar da munanen hare-hare a Nijar, abin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Tuni dai Kasashen Nijar da Najeriya da Kamaru da Chadi suka kaddamar da shirin kakkabe kungiyar Boko Haram da ta salwantar da rayukan al’umma da dama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.