Isa ga babban shafi
Nijar

Mayakan jihadi sun kai hari a gidan yarin Nijar

Rahotanni daga birnin jamhuriyar Nijar na cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari a sanyin safiyar yau a kan gidan yarin Koutou Kale mai tazarar kilomita 50 a yammacin birnin Yamai.

An tura karin jami'an tsaro don kai wa gidan yarin na Koutou Kale dauki
An tura karin jami'an tsaro don kai wa gidan yarin na Koutou Kale dauki ISSOUF SANOGO / AFP
Talla

Bayanai na nuni da cewa akwai alamar maharan masu da’awar jihadi ne kuma suna  kokarin ceto magoya bayansu da ke tsare a gidan yarin.

Wasu bayanan sun ce, an tura karin jami’an tsaro domin kai dauki ga jami’an da ke kula da gidan yarin, wanda shi ne mafi tsaro a duk fadin kasar ta Nijar.

Mafi yawa daga cikin wadanda ake zargi da ayyukan ta’addanci da aka kama a iyakar kasar ta Nijar da Mali da kuma ‘yan Boko Haram da aka kama a yankin Diffa, ana tsare da su ne a wannan gidan yari na Koutou Kale.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.