Isa ga babban shafi
CAF

Drogba da Mikel da Yaya Toure da Song suna cikin wadanda CAF za ta zaba gwarzon Afrika

Hukumar CAF da ke kula da kwallon kafa a Nahiyar Afrika ta fitar da jerin sunayen ‘Yan wasa 10 da zata zaba gwarzon Afrika a bana. ‘Yan wasan sun hada da dan wasan Kamaru Alexander Song da ke taka kwallo a kungiyar Barcelona a Spain. Akwai dan wasan kasar Ghana Andre Ayew da ke taka leda a kungiyar Marseille ta Faransa.

Dan wasan Cote d'Ivoire  Yaya Touré da dan wasan kasar Zambia Christopher Katongo
Dan wasan Cote d'Ivoire Yaya Touré da dan wasan kasar Zambia Christopher Katongo Reuters
Talla

Akwai kuma Christopher Katongodan dan wasan kasar Zambia da ke taka kwallo a kungiyar Henan Contruction ta kasar China. Sai kuma Demba Ba dan kasar Senegal da ke wasa a kungiyar Newcastle United.

Akwai sunan Didier Drogba na cote d’Ivoire da ke wasa a kungiyar Shaghai Shehua ta kasar China. Akwai kuma Lombe Yao Kouassi shi ma dan wasan Cote d’Ivoire ne da ke taka kwallo a kungiyar Arsenal ta Ingila.

Akwai dan Najeriya John Obi Mikel da ke taka kwallo a kungiyar Chelsea mai rike da kofin gasar zakarun Turai.

Akwai kuma Yaya Toure na Cote d’Ivoire da ke wasa a Manchester City wanda aka zaba gwarzon afrika a bara. Sai Younes Belhanda na Morroco da ke taka leda a kungiyar Montpellier ta Faransa.

Kafin karshen watan Nuwamba ne dai za’a tankade ‘Yan wasa bakwai a fitar da sunayen ‘Yan wasa uku wadanda cikinsu ne za’a zabi gwarzon Afrika a bana a watan Disemba a birnin Accra na kasar Ghana.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.