Kwallon Kafa
Diouf ya nemi Hukumar kwallon Senegal yin murabus
Tsohon dan wasan Senegal El Hadji Diouf ya yi kira ga gwamnatin kasar Senegal ta kori shugabannin hukumar kwallon kafa saboda rikicn da ya faru a birnin Dakar a wasan neman shiga gasar cin kofin Afrika tsakanin Senegal da Cote d’Ivoire. A cewar Diouf ya zama dole hukumar kwallon kafar kasar ta dauki alhakin aukuwar al’amarin da har ya yi sanadiyar dakatar da wasa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: