Brentford ta sayi wani matashin ɗan wasan Najeriya daga Kaduna
Brentford ta sayi ɗan wasan tawagar ƙasa da shekaru 20 na Najeriya Benjamin Frederick daga makarantar horos da ƴan wasan kwallon ƙafa na Moses Simon da ke Kaduna, a wata yarjejeniyar shekaru hudu.
Wallafawa ranar:
Ɗan wasan bayan mai shekaru 18 kachal ya amince ya koma ƙungiyar da ke doka gasar Premier ta Ingila.
Masanin harkokin wasannin kwallon kafar nan Fabrizio Romano ya ce dan wasan wanda ya je club ɗin amatsayin aro a bazara da nufin kaiwa ga ciniki, ya kulla yarjejeniyar shekaru hudu da Brentford. Ya gamu da dan wasan Najeriya Frank Onyeka a can.
Rahotanni sun ce Frederick ya ja hankalin kungiyoyin Turai irinsu Bayern Munich da Real Madrid da kuma FC Porto.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu