Isa ga babban shafi
Kenya

Kotu a Kenya ta umurci gwamnati ta bude gidajen Talabijin da ta rufe

Kotu a Kenya ta bayar da umurnin bude wasu gidajen talabijin da gwamnatin kasar ta rufe saboda nuna bikin rantsuwar kama aiki a matsayin shugaban kasa da jagoran ‘yan adawa Raila Odinga ya yi.

Wasu alkalai a  Nairobin Kasar Kenya
Wasu alkalai a Nairobin Kasar Kenya REUTERS/Baz Ratner
Talla

Kotun ta bayar da umurnin sake bude tashoshin ne kafin ta yanke hukuncin karshe a kai a cikin kwanaki 14 masu zuwa.

To sai dai kungiyoyin kare hakkin fadin albarkacin baki, na ganin cewa bai kamata a rufe wadannan gidajen talabijin ba, domin kuwa sun yi aikinsu ne na yada labarai.

Gidajen talabijin da aka rufe sun hada da NTV, Citizen TV da kuma KTN News.

A ranan larabar da ta gabata, Ministan cikin gida ya shaida cewar gidajen talabijin din zasu ci gaba da kasance wa a rufe har sai an kammala binciken da ake gudanar wa akansu.

Shima dai Ministan tsaron kasar Fred Matiang’i, ya zargi wasu kafafen yada labarai wajen taimakawa da ingiza rikici a kasar abinda kan iya janyo dubban mutane cikin hadari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.