'Yan Mata 4 Sun Kai Harin Kunar Bakin Wake A Kamaru
Wasu mata 4 ‘yar kunar bakin wake sun tasar da bama-bamai da ke jikinsu a garin Mora da ke arewacin kasar Kamaru, yankin da ke fama da hare-hare daga ‘yan kungiyar Boko Haram.
Wallafawa ranar:
Shaidu sun bayyana wa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa, matan sun tarwatsa kansu, inda kuma suka kashe wasu fararen hula da dama a wannan gari da ke dab da kan iyakar kasar ta Kamaru da Najeriya.
A garin Mora ake da cibiyar Sojan karo-karo na kasashe dake yakar ta'addanci kuma nan ne Sojan Kamaru ke da tarin makamai na yaki.
Majiyoyi na cewa 'yan matan na shirin kutsa kai cikin gari ne a lokacin da kungiyoyin sa kai suka gansu inda nan take 'yan matan suka tasar da bama-bamai da suka yi jigida da su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu