Boko Haram : Manoma na kauracewa gonakki a Borno
A dai-dai lokacin da rundunar sojin Nigeria ke ikirarin cewar tana samun gagarumar nasara a yakin da take yi da kungiyar Boko Haram, sai kuma ga dukan alamu wankin hula na shirin kaiwa dare. Domin manoma a garin Maiduguri na dari-darin zuwa gonakansu saboda yadda ‘yan Boko Haram ke kashe mutane tare da yin garkuwa da da wasu yayin da suke aiki a gonakkinsu.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A cikin ‘yan kwanakin baya-bayan nan mutane da dama suka rasa rayukansu yayin da wasu suka bata, a irin wannan yanayi, inda ake danganta faruwar hakan akan ‘yan ta’addar Boko Haram. Wakilinmu a Maiduguri Bilyamin Yusuf ya aiko da rahoto daga Maiduguri.
Boko Haram : Manoma na kauracewa gonakki a Borno
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu