Isa ga babban shafi
Turai

Juncker ya bukaci kasashen Turai su daina kyamar ‘yan ci-rani

Shugaban hukumar kungiyar Tarayyar Turai Jean-Claude Juncker ya bukaci gwamnatocin Turai su dai na kyamar ‘Yan ci-rani da ke ci gaba da tururuwa domin shiga kasashen.

'Yan ci-rani na bi ta barauniyar hanya domin shiga kasashen Turai
'Yan ci-rani na bi ta barauniyar hanya domin shiga kasashen Turai REUTERS/Pascal Rossignol
Talla

Juncker ya ce kasashen na da rawar da zasu taka wajen magance kwararar ‘Yan ci-ranin maimakon korarsu daga kasashen.

Yawancin ‘Yan ci-ranin dai ‘yan asalin Syria ne mai fama da rikici da kuma ‘yan Eritrea da ke ci gaba da kwarara ta mashigin Italiya da Girka.

A watan Oktoba ne dai mambobin kasashen Tarayyar Turai suka amince da matakin rarraba ‘yan ci-ranin kimanin 32,000 a tsakaninsu, amma har yanzu wasu kasashen sun ki karbar ‘Yan ci-ranin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.