Shirin 'Dandalin Nishadi' wanda ya saba zuwa muku a kowane mako ya taho da abubuwan ban nishadi, inda bayan ya leka masana'antar shirya fina-finai ta Kannywood, ya tattauna da mmawakin nan mai tashe, wanda ya rera wakar, 'Muradina', wato Ashiru Nagoma (Fasihi).
Sauran kashi-kashi
-
Aya Nakamura,da Gazo suka lashe kyautar mawakan shekara na Faransa
An gudanar da bikin bayar da kyaututuka ga mawakan zamani a birnin Paris na kasar Faransa, inda mawaka da suka yi fice kamar su Aya Daniocko da aka fi sani da sunan Aya Nakamura, da Ibrahim Diakite mai suna Gazo suka kasance a sahun gaba a wannan biki na mawaka a Faransa.27/04/202419:34 -
Ƙorafin Zango ya haifar da cece-kuce a ciki da wajen Kannywood
Shirin 'Dandalin Nishaɗi' na wannan mako tare da Abdoulaye Issa ya maida hankali kan wani batu da ya kare da shafukan sada zamunta wato kalaman da ɗay daga cikin jarumai a masana’antar fina-finai ta Kannywood Adam A Zango ya yi wanda ya fito tare da bayyana damuwa kan abin da ya kira butulci da aka masa, al’amarin da ya janyo martani daga da damacikin masu bibiyar masana’antar ta Kannywood. Sai kuma yadda ake shirin bikin kalankuwa na Femua da zai gudana a kasar Cote d’Ivoire.20/04/202420:12 -
Bangaren masana'antu zasu iya taimakawa wajen ci gaban tattalin arzikin Najeriya
Wannan bikin baje kolin fasaha karkashin inuwar Bankin Afirka, a karkashin sa ido da gudanarwa masana’anta da kuma wurin koyon ayuka na Soto Gallery ya shirya, yana baiwa matasa masu hazaka da fasaha damar samun horo na zamani da ya dace daga kowace kusurwa ta Najeriya.23/03/202420:10 -
Yadda jama’a ke ta bayyana ra’ayoyi kan fitar wani sabon shiri mai suna Matar Mai gari
Mai saurare a cikin shirin na wannan mako zaku ji yadda jama’a ke ta bayyana ra’ayoyi kan fitar wani sabon shiri mai suna Matar Mai gari wanda fitaciyyar jarumar fina-fina Saratu Daso ta shirya, Zamuji banbancin sa da sauran fina-finai.Akwai mu da rahoto na musamman kan mutuwar fitaccen mai wasan barkwancin nan na jamhuriyar Nijar wato Ada Mai Kano.09/03/202420:00 -
Babbar kotun jihar Kano ta yi umurnin a kamo mawaki Ado Gwanja
A cikin shirin na wannan mako zaku ji yadda babbar kotun jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta bada umarnin kamo mata fitaccen mawaki Ado Gwanja, sannan ta haramta masa waka har zuwa lokacin da za’a kammala shari’ar tuhume-ruhumen da ake yi masa.Akwai mu dauke da ci gaban tattaunawa da mawaki Abdallah Abdallah Muhammad da aka fi sani da Amdaz ko kuma Excellency.02/03/202419:59