Isa ga babban shafi
Nijar-Juyin Mulki

An kama sojojin da suka yi yunkurin juyin mulki a Nijar

An kama wasu sojoji bayan sun yi yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Nijar a sanyiin safiyar Larabar nan, yayin da aka dauki tsawon lokaci ana harbe-harben bindiga a babban birnin Yamai.

Wasu sojojin Jamhuriyar Nijar
Wasu sojojin Jamhuriyar Nijar U.S. Africa Command - Richard Bumgardner
Talla

Mazauna birnin sun ce, sun kwashe tsawon dare suna jin  karar harbe-harben bindiga a kusa da fadar shugaban kasar , al’amarin da ke zuwa a daidai lokacin da ya rage kwanaki biyu a rantsar da Bazoum Mohamed a matsayin sabon shugaban kasar.

Mazauna birnin sun ce, da misalin karfe uku na dare aka yi ta harbe-harbe da manya da kananan makamai, inda aka dauki tsawon minti 20 ana bude wuta.

Wata majiya da ta bukaci a sakaya sunanta ta ce,  tuni aka cafke sojojin da ake zargi da kitsa juyin mulkin da bai yi nasara ba.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Mohamane Ousmane ke ci gaba da ikirarin cewa, shi ya lashe zaben shugaban kasar zagaye na biyu da aka gudanar a ranar 2 ga watan jiya duk da cewa Kotun Fasalta Kundin Tsarin Mulki ta tabbatar da nasarar Bazoum.

Ousmane ya bukaci magoya bayansa da su gudanar da tattaki cikin lumana a sassan kasar, amma hukumomin Nijar sun haramta gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnati a ranar Laraba.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.