Isa ga babban shafi
Zaben Nijar

Kotu ta tabbatar da Bazoum a matsayin shugaban Nijar

Kotun Fasalta Kundin Tsarin Mulkin Jamhuriyar Nijar ta tabbatar da Bazoum Mohamed a matsayin sabon shugaban kasar wanda ya samu sama da  kashi 55 na kuri’un da aka kada a zagaye na biyu na zaben watan jiya.

Zabebben shugaban Jamhuriyar Nijar Bazoum Mohamed
Zabebben shugaban Jamhuriyar Nijar Bazoum Mohamed Niger Search
Talla

Wannan na zuwa bayan ‘yan adawa sun yi watsi da sakamakon zaben suna zargin an yi musu magudi, lamarin da ya haddasa kwarya-kwaryar tashin hankali har aka samu asarar rayukan mutane biyu a babban birnin Yamai.

Yanzu haka kotun ta ayyana cewa, daga ranar 2 ga watan Afrilun mai zuwa, Bazoum na da ikon jagorantar kasar ta Nijar a tsawon shekaru biyar.

Bazoum wanda tsohon Ministan Cikin Gida ne zai gaji shugaba Mahamadou Issofou mai barin gado wanda ya shafe wa’adi biyu na shekaru biyar-biyar kana karagar mulki.

A karon farko kenan da wani zababben shugaba ke mika mulki ga wani zababben shugaban daban tun bayan da kasar ta samu ‘yancinta daga turawan mulkin mallaka na Faransa a shekarar 1960.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.