Ambaliyar ruwa ta rutsa da mutane akalla 50,000 a Nijar
Mutane 22 suka mutu sakamakon ambaliyar da aka samu a Jamhuriyar Nijar bayan ruwan sama mai karfi wanda ya shafi mutane kusan 50,000.
Wallafawa ranar:
Alkaluman da hukumomi suka bayar sun nuna cewa gidaje 3,000 suka rushe, yayin da eka sama da 4,000 na gonaki suka lalace.
Yayin zantawa da sashin Hausa na RFI Ministan agajin gaggawa Lawan Magaji ya ce birnin Agadez na da wasu manyan duwatsu wadanda suke da akalla tsawon kilo mita 2 zuwa sama, wadanda daga nan ne idan aka samu saukar ruwan sama, ruwa ke gangarowa da karfin gaske lamarin da ke haddasa gagarumar ambaliyar ruwa ga duka karkarar da ya tarar.
Ministan agajin gaggawa na Jamhuriyar Nijar Lawan Magaji
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu