Isa ga babban shafi
Nijar

Manoma a Nijar na bukatar tallafin gaggawa don kafa kamfanin sarrafa albasa

Manoma da kuma masu sarrafa albasa a Jamhuriyar Nijar sun bukaci samun tallafin gwamnati domin fara aikin gina kamfanin sarrafa albasa na kasa da kasa a yankin Madawa da ke jihar Tawa wanda aka jima ana kokarin ganin samuwarsa.

Babbar kasuwar albasa  ta Galmi a Jamhuriyyar Nijar.
Babbar kasuwar albasa ta Galmi a Jamhuriyyar Nijar. abcburkina.net
Talla

A cewar shugaban wannan shiri Mustapha Kadri Sarkin Abzin, lokaci na ci gaba da tafiya kuma matukar ba a yi wani abu ba to gwamnati da manoman kasar Senegal za su iya shiga gaban Nijar wajen yin fice a aikin na sarrafa albasa.

Yayin zantawarsa da sashin hausa na RFI, sarkin Azbin, ya ce watanni hudu suka rage musu a dakon da ake wajen ganin gwamnatin Nijar ta bada kasonta na taimakon kudi don tabbatar da shirin gina kamfanin sarrafa albasa a yankin na Madawa karkashin tallafin wasu Faransawa. A cewarsa muddin wannan dama ta wuce su to fa zata koma ga kasar Senegal ko Burkina Faso.

00:59

NIGER-ONION-TRANSFORMATION-SCHEME-ABZIN-2017-04-12

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.