Isa ga babban shafi
Nijar

Malaman makaranta na yajin aiki a Nijar

Malaman makaranta a Jamhuriyar Nijar sun tsuduma a cikin yajin aikin gama gari a wasu manyan biranen kasar da suka hada da Yameh, Zinder, Maradi, Tahoua, domin neman ganin hukumomin kasar.

Shugaban kasar Jamhuriyyar Nijar Issoufou Mahamadou
Shugaban kasar Jamhuriyyar Nijar Issoufou Mahamadou today.ng/news/africa
Talla

Sai dai a wasu biranen kasar rahotanni sun ce ‘yan sanda sun tsare wasu shugabanin kungiyoyin malamai.

Malaman na yajin aikin ne saboda zargin taka hakkokin su.

Wani malami da ya nemi mu sakaya sunan sa ya tabbatar da gaskiyar halin da ake ciki yayin zantawarsa da sashin hausa na RFI.

A bayanin nasa ya jaddada cewa malaman zasu cigaba da kasancewa kan bakansu na cigaba da yajin aikin har sai gwamnati ta saurari bukatunsu.

01:02

Malaman makaranta a Nijar na yajin aiki

Nura Ado Suleiman

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.