Isa ga babban shafi
Nijar

An gano malaman makaranta na boge sama da 2,000 a Nijar

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa HALCIA ta ce ta gano malaman makaranta na boge 2,565 a cikin jahohi 5 na Jamhurriyar Nijar.

Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou.
Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou. AFP PHOTO / FAROUK BATICHE
Talla

Salissou Oubandoma mukadashin jagoran hukumar ya bayyana cewa a duk wata gwamnatin na biyan albashi ga malaman na boge dake cikin jahohin kasar 5 da suka hada Yamai da Dosso da Tahoua sai Agadez da kuma jahar Diffa.

Sauren jahohin 3 da suka hada da Zinder, Maradi, da Tillabery za a bayyana nasu sakamakon binciken na gaba.

An gudanar da binciken ne daga makaranta zuwa makaranta a Jamhuriyar Nijar Kashi 80% na malaman makaranta na aiki ne a karkashin tsarin kwantiragi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.