Isa ga babban shafi
Nijar

Kotun Ecowas ta bukaci kasar Nijar ta biya iyalen marigayi Ba'are diyya

Kotun kasashen yammacin Afirka Ecowas da ke birnin Abuja na tarayyar Najeriya, a yau juma’a ta bukaci hukumomi a jamhuriyar Nijar da su biya iyalan tsohon shugaban kasar Ibrahim Ba’are Mainasara diyya CFA milyan 435, sakamakon kisan da sojojin kasar suka yi masa a shekarar 1999.

Tsohon shugaban Nijar Ibrahim Baare Mainassara
Tsohon shugaban Nijar Ibrahim Baare Mainassara
Talla

Alkalan kotun da ta yanke wannan hukunci su biyar ne suka bukaci hukumomin kasar ta Nijar da su biya diyyar ta kwatankwanci Euro dubu 663, kimanin dalar Amurka dubu 750.

Kotun ta ce za a raba wa iyalan Ba'are da kudaden ne, inda matarsa za ta samu CFA milyan 75, kowanne daga cikin 'yayansa su biyar zai samu CFA milyan 50, yayin da za a raba sauran kudaden wato milyan 10 a tsakanin 'yan uwansa na jini su 11.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.