Isa ga babban shafi
Najeriya

Miliyoyin mutane za su bukaci agaji a Najeriya

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, kimanin mutane miliyan 14 ne za su bukaci agaji a yankin arerwa maso gabashin Najeriya mai fama da rikicin Boko Haram nan da shekara mai zuwa.

Wasu kananan yara da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu
Wasu kananan yara da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu
Talla

Majalisar ta kuma gargadi cewa, dubban kananan yara daga yankin na fuskantar barazanar mutuwa saboda yunwa.

Babban jami’in majalisar a Najeriya, Peter Lundberg ya shaida wa taron manema labarai cewa, akalla mutane miliyan 26 ne matsalar Boko Haram za ta shafa a shekara mai zuwa, in da miliyan 14 daga cikin su za su bukaci agaji ga kasashen duniya.

Mr. Lundberg ya kara da cewa, a halin yanzu akwai kananan yara dubu 75 da za su iya rasa rayukansu nan da wasu watanni masu zuwa matukar aka gaza ba su taimakon da ya dace.

Rikicin Boko Haram dai ya yi sanadiyar mutuwar mutane kimanin dubu 20 a cikin shekaru bakwai da suka gabata, tare da raba miliyoyi da gidajensu

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.