Isa ga babban shafi

Isra'ila ta janye dubban sojojinta daga kudancin Zirin Gaza

Rahotanni daga Zirin Gaza na cewa dubban sojojin Isra’ila sun janye daga kudancin yankin na Falasdinu, ciki har da birnin Khan Younis, inda suka shafe watanni suna fafatawa da mayakan Hamas.

Dubban Falasdinawan da suke kokarin komawa muhallansu a birnin Khan Younis bayan janyewar  dakarun Isra'illa daga kudancin Zirin Gaza. Falasdinawa sun kama hanyar komawa Khan Younis ne bayan dogon zaman gudun hijira da suka yi a garin Rafah. 7 ga Afrilu, 2024.
Dubban Falasdinawan da suke kokarin komawa muhallansu a birnin Khan Younis bayan janyewar dakarun Isra'illa daga kudancin Zirin Gaza. Falasdinawa sun kama hanyar komawa Khan Younis ne bayan dogon zaman gudun hijira da suka yi a garin Rafah. 7 ga Afrilu, 2024. AFP - MOHAMMED ABED
Talla

Matakin na zuwa a yayin da aka cika watanni 6 da barkewar yaki a yankin na Gaza.

Sai dai wani mai fashin baki kan sha’anin tsaro a Isra’ilar ya ce janye sojojin da ta yi daga  kudancin na Gaza ba ya nufin kawo karshen yakinta da Hamas ko kuma kusantar hakan, illa kawai dabarar sauya salon yakin.

A wani labarin kuma dubban ‘yan Isra’ila sun gudanar da zanga-zangar neman Fira Ministan kasar Benjamin Netanyahu yayi murabus, bisa zarginsa da gazawa wajen kare muradunsu.

Masu zanga-zangar sun kuma nemi a gaggauta kulla yarjejeniyar sulhun da za ta kai ga sako ragowar Yahudawan da mayakan Hamas ke garkuwa da su a Zirin Gaza.  

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.