Isa ga babban shafi
Syria

Kusan mutane 90 sun mutu yayin gumurzun mayakan IS da dakarun Kurdawa

Mutane kusan 90 sun rasa rayukansu bayan da aka kwashe akalla kwanaki uku ana gwabza fada tsakanin mayakan IS da dakarun Kurdawa a Syria, bayan da kungiyar ta IS ta kai hari kan wani gidan Yari, da aka tsare dubban mayakanta.

Mayakan Kurdawa a arewacin Syria.
Mayakan Kurdawa a arewacin Syria. © Goran Tomasevic/Reuters
Talla

Harin da aka kai gidan Yarin Ghwayran da ke birnin Hasakeh a arewa maso gabashin Syria, na daya daga cikin munanan hare-hare da mayakan IS suka kai a baya bayan nan, tun bayan ayyana fatattakarsu daga kasar kusan shekaru uku da suka gabata.

Shugaban kungiyar 'Syrian Observatory' da ke sa ido kan kare hakkin dan Adam a Syria, Rami Abdel Rahman, ya ce akalla jami'an tsaron Kurdawa 28, da fararen hula 5, da kuma mayakan IS 56 ne aka kashe, yayin gumurzun da aka shafe kwanaki uku ana yi.

Tun a ranar Alhamis IS ta kaddamar da farmaki kan gidan Yarin da ake tsare da wasu mayakanta da adadinsu ya kai akalla dubu 3 da 500, ciki har da wasu shugabanninta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.