Mayakan IS sun kashe jami'an tsaron Kurdawa 18 a gidan Yarin Syria
Jami’an tsaron Kurdawa akalla 18, ciki harda masu gadi, aka kashe a wani harin da kungiyar IS ta kai kan gidan yarin Syria da ke dauke da dubban mutanen da ake tuhumarsu da zama mayaka masu ikirarin jihadi.
Wallafawa ranar:
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria, ta ce jami’an tsaron Kurdawa sun samu nasarar kashe mayakan na IS akalla 16 a fadan da aka gwabza a daren ranar Alhamis a gidan yarin Ghwayran.
‘Syrian Observatory’ da ke sa ido kan yakin kasar Syria ta bayyana farmakin da IS ta kai gidan Yarin, a matsayin hari mafi muni tun bayan da aka shelar fatattakar 'yan ta'addan na IS cikin shekarar 2019 a kasar ta Syria.
Gidan Yarin Ghwayran da ke birnin Hassakeh a arewa maso gabashin Syria yana dauke da mutane kusan dubu 3,500 da ake zargin 'yan kungiyar IS ne da suka hada da wasu manyan shugabannin kungiyar, kuma fadan na ranar Juma'a ya zo ne a daidai lokacin da fursunonin na IS ke kokarin tserewa daga sansanin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu