Isa ga babban shafi
Syria

'Yan Syria sun kona litattafan Turkiyya saboda batanci ga Annabi

Wasu litattafai da Ma’aikatar Ilimi ta Turkiya ta samar tare da rarraba su a arewacin Syria, sun janyo fushin al’umma saboda yadda suke dauke da zanen kwatancen Annabi Muhammadu Sallahu Alaihi Wasallam, yayin da jama’a suka kona litattafan.

Wannan hoton da aka dauka daga jirgin sama a ranar 15 ga Mayu, 2020 yana nuna hoton yankin Ariha a kudancin lardin Idlib na kasar Siriya.
Wannan hoton da aka dauka daga jirgin sama a ranar 15 ga Mayu, 2020 yana nuna hoton yankin Ariha a kudancin lardin Idlib na kasar Siriya. © AFP
Talla

Al’ummar Musulmin duniya na girmama Annabi Muhammad, kuma suna daukar duk wani wargi da aka yi masa a matsayin gingimemen laifi ko kuma sabo.

Littafan na addini da Ma’aikatar Ilimin Turkiya ta wallafa domin ilmantar da yara a wasu yankuna na Syria dake karkashin ikon gwamnatin Ankara, na dauke da zane-zanen da jama’ar yankin suka bayyana a matsayin cin mutuncin addini.

A can birnin Jarablus, kusa da kan iyakar Turkiya,  jama’a sun kona daukacin littafan da suka zo hannunsu kurmus kamar yadda wasu fayafayen da aka watsa a shafukan sada zumunta suna nuna.

Daya daga cikin mazauna yankin na Jarablus, Mustafa Abdulhaq ya ce, lallai sun kadu matuka da ganin wadannan littafai masu munin gaske, dalilin ya sa suka kona su a cewarsa.

Kazalika al’ummar birnin Al-Bab sun lashi takobin gudanar da zanga-zanga a yau Juma’a mudin ba a shafe wadannan kazaman littafai baki daya ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.