Isa ga babban shafi

Hadaddiyar Daular Larabawa ta dauki nauyin ginawa Afirka ta Tsakiya sabon filin jirgi na zamani

A jamhuriyar Tsakiyar Afrika,wata tawagar kungiyar kasashen Brics da ta ziyarci wannan kasa ta cimma yarjejeniya da hukumomin kasar na sake fasalta wasu daga cikin manyan ayuka da suka jibanci sufuri,sadarwa.

Birnin Bangui na kasar Afirka ta Tsakiya
Birnin Bangui na kasar Afirka ta Tsakiya Getty Images - mtcurado
Talla

Ministan Sufuri Afrika ta Tsakiya, Herbert Gontran Djono Ahaba, da Shugaban kasar Faustin Archange Touadéra, sun bayyana farin cikin su ganin ta yada aka cimma yarjejeniya na  gina sabon filin jirgin sama a babban birnin Bangui, aikin da  Hadaddiyar Daular Larabawa ta dauki nauyin sa.

Filin tashi da saukar jiragen Bangui
Filin tashi da saukar jiragen Bangui © Charlotte Cosset/RFI

Hukumomin na  Afirka ta Tsakiya zasu samar da fili mai fadin hekta dari uku domin gina wannan sabon filin jirgin a wajen Bangui, yayinda ake bayyana cewa  Masarautar daular Larabawa za ta ware kudi zuzzurutu dalar Amurka miliyan 200, sama da CFA biliyan 120 dangane da wannan aiki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.