Isa ga babban shafi

An gudanar da zanga-zangar adawa da sauya kundin mulki a Afirka ta Tsakiya

Daruruwan ‘yan kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ne suka bijirewa dokar hana fita jiya Jumma’a suka   gudanar da zanga-zanga a birnin Bangui don nuna adawa da shirin sauya kundin tsarin mulkin kasar.

Wasu masu zanga-zangar adawa da fasalta kundin tsarin mulki a Bangui na jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.
Wasu masu zanga-zangar adawa da fasalta kundin tsarin mulki a Bangui na jamhuriyar Afirka ta Tsakiya. AFP - BARBARA DEBOUT
Talla

Gamayyar jam'iyyun adawa ta "Republican Bloc for the Defence of the constitution” ce ta shirya tattakin.

Babban sauyi dake cikin daftarin fasalta kundin tsarin mulkin dai zai bada dama shugaban kasa ya yi ta mulki har tsawon rayuwarsa, wanda zai kawo karshen wa'adi 2 da shugaban kasa ke yi a halin yanzu.

'Yan adawar sun jagoranci wani tattaki na kusan mutane 500 karkashin rakiyar jami'an tsaron kasar da motocin sulke da tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya MINUSCA ta girke, kamar yadda 'yan jaridar AFP suka shaida.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.