Isa ga babban shafi

Na hannun daman Laurent Gbagbo, Charles Ble Goude ya samu izinin komawa gida

Tsohon na hannun daman shugaban kasa a lokacin mulkin Laurent Gbagbo na Ivory Coast wato Charles Ble Goude ya shaidawa kamfanin dilancin labaran Faransa na AFP cewa zai koma gida a wata mai zuwa domin shiga cikin shirin sulhun kasar, bayan da aka wanke su daga laifukan cin zarafin bil adama.

Tsohon shugaban kasar Ivory Coast Laurent Gbagbo.
Tsohon shugaban kasar Ivory Coast Laurent Gbagbo. AFP - ISSOUF SANOGO
Talla

Shugaban Ivory Coast Alassane Ouattara ne ya amince da ranar ta 26 ga watan Nuwamba, a matsayin ranar da Ble Goude zai koma gida.

Tsohon shugaba Gbagbo kuwa ya koma gida Abidjan ne a watan Yunin shekarar 2021 amma Ble Goude ya jira har sai da fadar shugaban kasa ta bashi dama.

A watan Maris na shekarar 2021, kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta wanke Ble Goude da Gbagbo daga laifukan cin zarafin bil adama yayin rikicin siyasar da ya barke a Ivory Coast a shekarar 2010-2011, bayan da Laurent Gbagbo ya ki amincewa da shan kaye a zaben da Ouattara yayi nasara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.