Isa ga babban shafi

Laurent Gbagbo ya kaddamar a sabuwar jam'iyya a Cote d'Ivoire

Tsohon Shugaban kasar Cote D’Ivoire Laurent Gbabgbo da ya dawo kasar a watan yunin shekarar bana bayan share kusan  shekaru 10 a tsare,a yau asabar  ya kudiri aniyar kafa sabuwar jam’iyya mai suna  PPA-CI wato jam’iyyar al’umar Afrika ta Cote D’ivoire.

Tsohon Shugaban kasar Cote D'Ivoire
Tsohon Shugaban kasar Cote D'Ivoire © REUTERS - MACLINE HIEN
Talla

Shirin na tsohon Shugaban kasar na zuwa a dai dai lokacin da magoya bayan sa ke shirya taron szamar da wannan jam’iya a birnin Abidjan ,inda kusan magoya baya da wakilai 1.600 za su rattaba hannu tareda yin na’am  wajen samar da wannan jam’iyya da za agoga da ita a zaben kasar na shekara ta 2025.

Tsohon shugaban Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo
Tsohon shugaban Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo REUTERS - LUC GNAGO

A wannan taro da za rufe gobe lahadi ,maid akin tsohon Shugaban kasar Simone Gbagbo wacce ta taka muhimiyar rawa  wajen samar da jam’iyyar farko ta Shugaba Gbagbo wato FPI a shekara 1982  ,ba ta halaraci zaman ba  bisa dalilai, inda wasu rahotanni ke dada nuni cewa ta na ziyara Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo yanzu haka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.