Gbagbo da Ble Goude na iya komawa gida -Ouattara
Shugaban Cote d’Ivoire Alassane Ouattara, ya ce tsohon shugaban kasar Laurent Bagbo da kuma jagoran matasa ‘yan gani-kashe-ni da ke mara masa baya wato Charles Ble na iya komawa gida a duk lokacin da suke bukata, bayan da kotun duniya ta ICC ta wanke su daga laifufukan da ake zarginsu da aikatawa.
Wallafawa ranar:
Shugaba Ouattara, wanda ke jagorantar taron majalisar ministocin kasar a wannan laraba, ya ce bayan dawowarsa a gida tsohon shugaba Laurent Bagbo zai ci moriyar illahirin hakkokin da doka ta ce a bai wa tsohon shugaban kasar.
A game da daukar nauyi da kuma dawainiyar tsohon shugaban da iyalansa domin komowa gida kuwa, shi ma wannan zai fito ne daga Baitul-malin kasar a cewar shugaba Ouattara.
To sai da shugaban kasar bai bayyana makomar hukuncin daurin shekaru 20 da wata kotu ta yanke wa Laurent Bagbo bayan samun sa da hannu a fashin da aka kai wa bankin kasashen yammacin Afirka na BCEAO kuwa lokacin da ake tsakiyar yakin basasar kasar ba.
A ranar 31 ga watan jiya ne kotun ta ICC ta wanke Laurent Bagbo da kuma Charles Ble goude daga illahirin zarge-zargen da ake yi masu, matakin da ke share masu fagen komawa gida Cote d’Ivoire idan suna bukata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu