Boko Haram ta kashe mutane 6 a Dikwa
Mayakan Boko Haram sun kashe mutane biyar tareda yin awon gaba da wasu can daban a wani kazamin hari da suka kai garin Dikwa dake da nisan kilometa 90 da Maiduguri a jihar Borno.
Wallafawa ranar:
Mutanen da harin ya ritsa da su na daga cikin mutanen da suka shiga dajin wajen neman itacen girki, yan boko Haram sun ritsa da su inda nan take suka kashe mutane biyar a cewar Babakura Kolo memba ne a kungiyar yan sa kai.
Garin Dikwa ya kasance wanin sanssani da aka girke yan gudun hijira dubu 70 da matsallar tsaro ya tilastawa baro matsugunin su da kuma ke rayuwa a karkashin kungiyoyin agaji.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu