Isa ga babban shafi
Benin

Ana Zaben Shugaban Kasar Benin Yau Lahadi

A yau lahadi al’ummar janhuriyar Benin ke gudanar da zaben shugaban kasa zagaye na biyu, inda ake fafatawa tsakanin Firaministan kasar mai-ci Lionel Zinsou da kuma Patrice Talon.

Fira Ministan kasar Benin Lionel Zinsou, kuma dan takara a zaben na Yau
Fira Ministan kasar Benin Lionel Zinsou, kuma dan takara a zaben na Yau REUTERS
Talla

Abdoulkarim Ibrahim Shikal wanda yanzu haka ke a birnin Cotonou fadar gwamnatin kasar ta Benin, ya ce an bude tashoshin zabe tun misalin karfe 7 na safe agogon kasar.

Ana sa ran a rufe rumfunan zabe da misalin karfe 4 na yamma.

Sakamakon farko na zaben za’a gabatar ne nan da kwanaki hudu.

Al'ummar kasar miliyan  hudu da dubu dari bakwai na zaben wanda zai maye gulbin shugaba mai barin gado ne Thomas Boni Yaya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.