Isa ga babban shafi
Kenya-AU-ICC

Kotun hukunta laifukan yaki ta ICC ta mayarwa shugabannin Afrika da martani

Babbar mai gabatar da kara a kotun hukunta laifukan yaki ta ICC, ta mayar da martani ga zargin da wasu shugabannin Afrika suka yi akan kotun tana nuna wariya a wajen gudanar da ayyukanta.

Babbar mai shigar da kara a kotun hukunta laifukan yaki ta ICC, Fatou Bensouda
Babbar mai shigar da kara a kotun hukunta laifukan yaki ta ICC, Fatou Bensouda REUTERS/Thomas Mukoya
Talla

Fatou Bensouda ta ce wadanda suke zargin suna kokarin kare shugabannin da a ke zargi da aikata laifukan yaki ne.

“Duk munsan wadanda ke wannan korari.” Inji Bensouda.

A yanzu haka kotun ta ICC na samun matsain lamba akan tuhumar shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta da mataimakinsa, William Ruto bisa zargin keta hakkin bil adama a lokacin da kasar ta fada rikici bayan zaben shekarar 2007.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.