Isa ga babban shafi
ICC-Congo-Rwanda

Kotun ICC ta bukaci a mika Ntaganda zuwa Hague

Kotun hukunta laifukan yaki ta ICC ta yi kira  a hannunta Kwamandan ‘Yan tawayen Jamhuriyyar Congo Bosco Ntaganda zuwa Hague bayan ya mika kansa ga ofishin jekadancin Amurka a birnin Kigali.

Janar Bosco Ntaganda, Kwamandan 'Yan tawayen Congo
Janar Bosco Ntaganda, Kwamandan 'Yan tawayen Congo © CPI
Talla

Ntaganda da ake kira da sunan "The Terminator", ana tuhumarsa ne da aikata laifukan yaki da cin zarafin bil’adama guda bakwai da suka hada da kisa da fyde da sa aikin bauta da kuma tursasawa yara shiga aikin Soji a kasar Jamhuriyar Congo.

A ranar Talata ne Ntaganda, mai shekaru 40 ya mika kansa ga ofishin jekadancin Amurka a Rwanda da ke makwabtaka da Jamhuriyyar congo.

Sai dai gwamnatin kasar Rwanda ta yi watsi da bukatar ICC, tana mai cewa wannan ya shafi Amurka da Gwamnatin Congo da kuma ICC.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.