Isa ga babban shafi
China-Najeriya

China ta yi kiran daukar matakin gaggawa a Najeriya bayan bindige ma’aikacinta

Gwamnatin kasar China ta yi Allah Waddai da kisan wani ma’aikacin kasar da aka bindige a Maiduguri tare da kiran mahukuntan Najeriya daukar matakin gaggawa domin kare rayukan ‘Yan kasashen Waje.

Hedikwatar 'Yan Sandan Najeriya a garin Maiduguri
Hedikwatar 'Yan Sandan Najeriya a garin Maiduguri AFP/Pius Utomi Ekepei
Talla

A ranar Juma’a ne wasu ‘Yan bindiga suka bindige wani ma’aikacin Kamfanin kasar China a birnin Maiduguri wanda shi ne mutum na biyu dan kasar China da aka kashe.

Kakakin ma’aikatar harakokin wajen China Hong Lie ya ce sun dauki wannan al’amarin da muhimmci matuka. Tuni kuma ofishin jekadancin China ya mika takardar koke ga gwamnatin Najeriya da ke kira ga gwamnatin kasar daukar matakin gaggawa.

A ranar Bakwai ga watan Oktoba wasu ‘Yan bindiga sun kashe wani dan China a garin Gubio da ke kusa da Maiduguri.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.