Kotu ta goyi bayan mika tsibiran Masar 2 ga Saudiyya
Kotun kolin Masar ta sake tabbatar da yarjejeniyar kasar ta cimma da Saudiya, na mika mata tsibiran Tiran da Sanafir, da masu adawa da matakin ke kallon tamkar Masar din ta mika wani yankinta mai tasirin Siyasa ne ga Saudiya.
Wallafawa ranar:
A watan Afrilun shekarar 2016 aka cimma yarjejeniyar tsakanin Saudiya da Masar, a lokacin ziyarar Sarki Salman wanda shi kuma ya sanar da shirin bai wa Masar din taimkon bashi da zuba hannun jari a kasar.
Yarjejeniyar ta haddasa zanga-zanga a sassan kasar, inda ‘yan adawa ke zargin gwamnatin Masar da sabawa kundin tsarin mulki, wanda ya haramtawa kasar mika wani yanki na iyakarta ga wata kasa.
Hukuncin kotun kolin ya ce yarjejeniyar mika tsabiran na Tiran da Sanafir ga Saudiyya, bai sabawa tsarin mulkin kasar ba.
Kafin zuwan wannan lokacin gwamnatin Masar ta yi ikirarin cewa asalin tsibiran biyu mallakin Saudiya ne, da ta mika wa Masar a matsayin aro cikin shekarar 1950.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu