Kotu ta tura Bala Muhammad gidan yarin Kuje
Wata kotun Tarayya a Abuja Najeriya ta tura Bala Muhammad zama a babban gidan yarin Kuje kan tuhumarsa da aikata laifukan rashawa a lokacin da yana ministan Abuja.
Wallafawa ranar:
Hukumar EFCC da ke yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ne ta maka tsohon ministan na Abuja a kotu kan cajinsa da aikata laifuka shida da suka kunshi sama da fadi da kudi Naira Miliyan 550.
Sannan ana zarginsa da rashin bayyana wasu kadarorin da ya mallaka. Amma Bala ya musanta dukkanin zargin.
Sai a ranar 12 ga Mayu ne Kotu za ta sake sauraren karar tsohon ministan inda za ta yanke hukuncin ba da shi beli.
Amma yanzu zai ci gaba da zama a gidan yarin Kuje har zuwa 12 ga wata.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu