Isa ga babban shafi
Eritrea-Habasha

Eritrea na takun-saka da Habasha

Hukumomin Eritrea sun zargi Habasha da kai hari kan sansanin sojinta da ke kan iyaka da kasashen biyu ke rikici da juna.

Shugaban Eritrea Isaias Afwerki
Shugaban Eritrea Isaias Afwerki madote.com
Talla

Ma’aikatar yada labaran Eritrea ta ce dakarun Habasha sun kai harin ne a Yankin Tsorona, sai dai mai Magana da ywun gwamnatin Habasha Getachew Redda ya ce ba su da labarin wata taho mu gama da aka yi.

Eritrea ta samu ‘yancin kai daga Habasha a shekarar 1991 bayan sun shafe shekaru suna yaki da juna.

Kuma ko bayan samun ‘Yancin kan Eritrea, sun sake gwabza yakin shekaru biyu tsakanin shekarar 1998 zuwa shekara ta 2000.

Kasashen dai na rikici ne kan garin Badme da ya yi iyaka da kasashen biyu wanda Majalisar Dinkin Duniya ta ba Eritrea amma har yanzu yana karkashin ikon Habasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.